11 Disamba 2021 - 13:39
Iran: Rahotannin Karya Ba Za su Raunana Aniyar Kasar Ta Kare Hakkokin Al’ummar Ta Ba

Babban mai shiga tsakanin na kasar Iran a tattaunawar da ake yi a birnin Biyanna ya kara jaddada kyakyawar niyar Iran na ganin an cimma matsaya a tattaunawar da take yi tsakaninta da kasashen turai 4 gami da kasar Jamus, na ganin an cire mata takunkumai, kana ya ce rahotanni karye da ake watsawa daga wajen dakin taron ba zai sanyaya guiwar kasar Iran ba.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - Bagheri Khani mataimakin ministan harkokin wajen Iran kan harkokin siyasa ya fadi cewa: “ Yarjejeniyar nukiliya da aka fi sani da suna JCPOA tana raye saboda aiki nauyin da ya rataya a wuyanta da Iran take yi.

A na sa bangaren wanda ke jagorantar tawagar kasar Rasha a tattaunawar ya ce : “ Iran da sauran kasashen turai 4 wato Birtaniya Faransa, Rasha da China gami da kasar Jamus suna aiki akan daftarin kudurin da iran ta mika musu a wajen zaman.

342/